AhlulBayt News Agency

source : Alumni.miu.ac.ir
Wednesday

23 December 2015

1:23:49 PM
726472

Full Text;

Second Message of Ayatollah Khamenei to the Western Youth in Hausa

Second Message of Ayatollah Khamenei to the Western Youth in Hausa.

Abin da ke biye fassarar wasikar da Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya aike wa matasan kasashen Yammacin Turai biyo bayan harin ta'addancin da aka kai kasar Faransa ne:

Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin Kai 

Ga Dukkanin Matasan Kasashen Turai

Abubuwa masu sosa rai da suka faru biyo bayan harin ta'addancin rashin imani da ya faru a kasar Faransa, shi ne ya sake sanya ni yin magana da ku, Ya ku matasa. Lalle abin bakin cikin ne a gare ni yadda irin wadannan abubuwan ne suke share fagen tattaunawa, to amma hakikanin lamarin shi ne cewa matukar wannan lamari mai bakanta rai bai share fagen samar da mafita da kuma yin tunani bai daya (na magance wannan matsalar) ba, to kuwa za a fuskanci hasara ninkin ba ninkiya. Cutuwa da wahalar kowane irin mutum, a ko ina yake kuwa a duniyan nan, a kan kanta wani abin bakin ciki da sosa ran bil'adama ne. Ganin karamin yaro yana magagin mutuwa a gaban masoyansa (iyaye ko ‘yan'uwansa), ko mahaifiyar da ta mayar da farin cikin iyalanta zuwa ga wani yanayi na juyayi, ko mijin da ke dauke da gawar matarsa a guje zuwa wani waje ko kuma dan kallon da bai san cewa nan gaba kadan ko zai ci gaba da rayuwa ko a'a ba, ko shakka irin wadannan yanayi ne masu sosa rai da zukatan mutane. Duk mutumin da yake da komai kashin kauna da dan'adamtaka, lalle zai tasiransu da kuma jin zafin ganin irin wannan yanayin, shin hakan a Faransa ne ya faru ko kuma a Palastinu ko Iraki ko Labanon ko Siriya. Ko shakka babu musulmi biliyan guda da rabi (na duniya) suna jin irin wannan zafin, sannan kuma suna gaba da kuma kiyayya da masu aikata wannan danyen aiki da kuma masu daure musu gindi. To amma lamarin shi ne cewa matukar irin wadannan cutarwa da wahalhalu ba su zamanto dalilin da za su sanya a gina gobe (makoma) mai kyau da kuma wacce tafi tsaro da kwanciyar hankali ba, to kawai za su zamanto mujarradin tunanin abubuwan da suka faru masu sosa rai kana kuma maras amfani ne. Ni na yi amanna da cewa ku din nan matasa kawai, ku ne ta hanyar daukar darussa daga abubuwa marasa kyau da suke faruwa a halin yanzu, za ku iya samar da sabbin hanyoyin gina gobe da kuma kawo karshen irin mummunar hanyar da ta kai kasashen yammaci zuwa ga tsaka mai wuyan da suka shiga ciki.

Ko shakka babu a yau ta'addanci ya zamanto wata cuta da bala'i da muka yi tarayya cikinsa, mu da ku, to amma ya zama wajibi ku san cewa akwai manyan bambanci guda biyu na asali tsakanin rashin tsaro da zaman dardar din da kuka shiga ciki sakamakon harin baya-bayan nan, da kuma wahalhalun da al'ummomin kasashen Iraki, Yemen, Siriya da Afghanistan suke ciki tsawon shekaru. Na farko shi ne cewa kasashen musulmi sun jima ainun cikin irin wannan tashin hankali da fuskantar ayyukan ta'addanci ta bangarori daban-daban. Na biyu kuma abin bakin cikin shi ne cewa irin wannan tashin hankali da kashe-kashe sun kasance ne karkashin kula da kuma goyon bayan wasu manyan kasashen duniya ta hanyoyi daban-daban. A yau dai da kyar za ka sami mutumin da ba shi da masaniya kan hannun da Amurka take da shi wajen kirkira ko kuma karfafawa da ba ka makamai ga kungiyoyin Al-Ka'ida, Taliban da sauran ‘yan amshin shatansu. Baya ga wannan goyon baya na kai tsaye, har ila yau kuma sun kasance kawaye kuma masu goyon bayan (kasashen) da suke goyon bayan (kungiyoyin) ‘yan ta'adda masu kafirta musulmi duk kuwa da tsarin kama-karya da suke gudanarwa a (kasashensu), alhali suna ci gaba da takurawa da kuma matsin lamba wa masu riko da mafi ci gaban tsarin da ya samo asali daga tsarin demokradiyya a wannan yankin. Siyasa da mu'amalar harshen damo da kasashen yammaci suke yi da kungiyoyi masu neman ‘yanci a duniyar musulmi wani babban misali ne na irin karo da juna da ake samu cikin siyasar kasashen yammaci.

Wata fuska da take nuni da irin wannan karo da juna (cikin siyasar kasashen Yammacin) ita ce goyon bayan da ake nunawa ta'addancin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra'ila. Mutanen Palasdinu da ake zalunta sun fuskanci mafi munin nau'oi na ta'addanci tsawon shekaru sittin din da suka gabata. Idan har a yanzu mutanen Turai sun buya a cikin gidajensu na wasu kwanaki da kuma nisantar shiga cikin taruka, to shekaru aru-aru kenan iyalan Palasdinawa hatta a cikin gidajensu ba su da aminci daga kisa da ta'addancin sojojin gwamnatin Sahayoniyawa. Da wani irin amfani da karfi da kuma kekashewar zuciya ce a yau za a iya kwatanta ta da gine-ginen matsagunan yahudawa ‘yan share wuri zauna da sahayoniyawa suke yi? A kowace rana wannan haramtacciyar hukumar tana ruguza gidajen Palastinawa da gonaki da lambunansu, amma ba tare da kawayenta masu tasiri a kanta sun ladabtar da ita, ko kuma alal akalla daga wajen kungiyoyin kasa da kasa wadanda suke ikirarin ‘yanci ba. Suna yin hakan ne kuwa ba tare da sun ba su damar tattara kayansu ko amfanin gonansu ba. Haka nan kuma a mafi yawan lokuta wadannan abubuwan na nuna kekeshewar zuciya suna faruwa ne a idanun mata da kananan yara da suke cikin fargita, wadanda suke ganin yadda ake dukan iyalansu da kuma yadda ake tafiya da su wajen azabtarwa. Shin ko kun san wata kekashewar zuciya kuma ta tsawon lokaci irin wannan?

Idan kashe mace akan titi saboda kawai ta nuna turjiya ga sojan da ya yi jigida da makamai ba ta'addanci ba ne, to mene ne? Saboda sojojin wata daula ce ta mamaya ta ke aikata wannan irin dabbancin, don haka bai kamata a kira shi wuce gona da iri ba? Ko kuma watakila saboda an dauki shekaru 60 ana maimata nuna hotunan wannan abin ne a talbijin shi ya sa ya zama ba ya motsa zukatanmu?

Hare-haren soji a kan kasashen musulmi cikin shekarun bayan nan, wadada suka sanadiyyar mutuwar wani adadi mai yawa na mutane, wani misali ne na daban na karo da junan da ke cikin tunanin kasashen Yammaci.Kasashen da aka kai wa harin, baya ga dimbin asarar rayukan al'ummominsu da suka yi, har ila yau kuma sun fuskanci hasarori ta bangaren cibiyoyin tattalin arziki da masana'antu. An kawo musu tsaiko da cikas a bangaren ci gaban kasa. Ta wasu fuskokin ma an mai da su baya na shekaru masu yawa. Amma duk da haka ana bukatarsu da kada su dauki kansu a matsayin wadanda aka zalunta. Ya za a ce kasar da aka rusa sannan kuma aka mai da biranenta zuwa kufai, amma kuma a bukace su kada sa dauki kawukansu a matsayin wadanda aka zalunta? Ashe maimakon ace an bukaci shafe musifun da suka faru, bai dacewa a nemi gafara ba? Wahalhalun da kasashen musulmi suka fuskanta cikin shekarun bayan nan ta hanyar munafuncin mahara da kokarinsu na wanke bakaken ayyukansu, bai gaza asarar abin duniya da aka yi ba.

Ya ku matasa! Ni ina da fatan cewa - a yanzu ko a nan gaba- za ku sauya wannan gurbataccen tunanin na yaudara, tunanin da aka gina shi bisa boye bakaken manufofi na nesa da yin ado wa munanan manufofi. A ganina matakin farko na samar da tsaro da kwanciyar hankali shi ne yin gyara da kuma daidaita wannan tunani da ke jawo tashin hankali. Matukar dai siyasar harshen damo ta kasashen Yammaci za ta ci gaba da jagoranci, kuma matukar masu goyon baya da daukar nauyin ta'addanci za su ci gaba da raba shi zuwa gida biyu, "mai kyau" da "mara kyau", sannan kuma matukar za a ci gaba da fifita amfani na gwamnatoci sama da manufofi na ‘yan'adamtaka, to bai kamata a nemi warware matsalar da ake kuka a kanta a wani wuri na daban ba.

Abin ban takaici shi ne wannan salon ya dauki tsawon shekaru yana samun gindin zama cikin siyasar kasashen Turai, ta yadda ya haifar da mummunar illa a boye. Da dama daga cikin kasashen duniya suna alfahari da al'adunsu na iyaye da kakanni, al'adun da suka karfafa kyakyawar dangantaka a tsakanin al'ummomin bil adama. Duniyar musulmi ma ba a bar ta a baya ba ta wannan fuskar. Amma a yau kasashen yammaci suna amfani da irin ci gaban da suka samu na zamani wajen rusa al'adu da kyawawan dabi'un sauran al'ummomin duniya ko ta wace hanya. Ni ina ganin kallafa al'adun yammacin duniya a kan sauran al'ummomi, da tozarta al'adu masu ‘yanci da asali, shi kansa wani bangare ne na haifar da fitina, domin kuwa yana tattare da cutarwa ga al'ummomi. Tozarta manyan al'adu da koyarwar al'ummomi da wasu bangarori na abubuwan da suke girmamawa kuwa, yana zuwa ne a daidai lokacin da al'adun da ake son a maye gurbinsu da su ko alama ba su cancanci hakan ba ko ta wace fuska. A matsayin misali,"cin zali" da "rashin kyakkyawar dabi'a", wadanda abin takaici sun zama muhimman abubuwan da aka gina al'adun kasashen Yammaci a kansu, karbuwarsu hatta a tsakanin al'ummomin wadannan kasashe tana raguwa matuka. Abin tambaya a nan shi ne: shin mun yi laifi idan muka ce ba mu son wata al'ada maras kyau da ma'ana? Shin mun yi laifi idan muka hana shigowar wasu al'adu masu yaduwa a tsakanin matasa da rusa tarbiyarsu? Ni ba ina musun muhimmanci da matsayin musayen al'adu ba ne. A duk lokacin da aka sami irin wannan musayen al'adu cikin yanayi na dabi'a da aka saba da shi da kuma girmama juna, to kuwa za a samu ci gaba da kuma karuwar dukiya. Amma idan a ka karbi al'adu marassa dacewa da yanayin al'umma su kan zama dalili na babbar asara.

Dole ne cikin dukkanin takaici da bakin ciki mu fadi cewa, kungiyoyi irin su Da'esh (ISIS) sakamako ne na irin al'adun da aka shigo da su aka kuma shuka su suka tsiro a cikin al'umma. Domin kuwa idan da abin da wadannan mutane suke yi yana da alaka ne da akida, to da an ga irin hakan tun kafin kunnowar ‘yan mulkin mallaka a duniyar musulmi, alhali tarihi yana nuna sabanin hakan ne. Akwai dalilai masu tarin yawa na tarihi da suke bayyawa a fili yadda alaka da haduwa tsakanin ‘yan mulkin mallaka masu tsattsauran ra'ayi da wuce gona da iri da kuma tunani na koma baya da kwakwalwar wata kabilar (larabawan) kauye, ta haifar da tushen tsaurin ra'ayi da wuce gona da iri a yankin nan. Idan ba haka ba, ta yaya zai yiwu daya daga cikin addinan da suka fi koyar da dan'adam kyawawan dabi'u da ‘yan adamtaka, wanda a cikin matanin kundinsa ya bayyana cewa kashe ran mutum daya daidai yake da kashe dukkanin ‘yan adam, amma kuma har a samu wata shara kamar (kungiyar) Da'esh ta fito daga wannan addinin?

A daya bangaren dole ne a yi tambayar cewa: Ya ya aka yi mutanen da aka haifa a nahiyar Turai, suka girma a can da kuma tunanin addini irin na can kuma suke shiga cikin irin wadannan kungiyoyi? Shin zai yiwu kuwa a amince da cewa saboda tafiya sau daya ko sau biyu zuwa wani wajen da ake fama da yaki kawai sai kawai mutum ya koma ya zama mai tsaurin ra'ayin da zai iya ruwan harsasai a kan ‘yan'uwansa? Tabbas bai kamata a manta da tasirin rayuwa cikin al'adu marassa kyau da kuma gurbatacciyar zamantakewa da ke haifar da bakin hali na son tashin hankali ba. A nan dole ne a yi bayani, bayanin da zai fito da abin da aka boye a cikin rayuwa ta zamantakewa. Mai yiwuwa akwai kiyayya mai zurfi da take komawa zuwa ga lokacin da turawa suke kokarin mikewa ta fuskar bunkasa tattalin arziki da masana'antu, sakamakon nuna bambanci da wariya a tsakanin mutane da rashin adalci ta fuskar shari'a, wanda ya sanya wasu zukatan suke dauke da wannan haushi da takaici, kuma wani abu mai sosa zuciya zai iya tayar da tsohon takaici.

Ko ma dai yaya lamarin yake, ku ne ya zama wajibi a kanku ku warware zaren da ya yi muku dabaibayi. Ku cire duk wani kulli da ke cikin ranku. Maimakon kara zurfafa baraka sai ku dunke ta. Babban kure da aka tafka a kan batun yaki da ta'addanci shi ne matakan martanin gaggawa, wanda kuma shi ne ya kara fadada barakar dake akwai yanzu. Duk wani yunkuri da zai saka musulmi mazauna nahiyar Turai da Amurka wadanda yawansu ya kai miliyoyi a cikin kunci da takura, kuma da ci gaba da tauye musu hakkokinsu na zamantakewa a cikin al'umma fiye da lokutan baya, tare da mayar da su saniyar ware a cikin al'umma, hakan ba wai kawai ba zai warware matsalar ba ce, a'a zai jawo wata baraka ne tare da kara fadada ta.

Daukar duk wani mataki da martani musamman idan lamarin ya shafi bangaren doka, baya ga kara rabuwar da ke akwai da kuma bude wasu kofofi ga wasu rikice-rikice a nan gaba babu abin da zai haifar. Bisa ga rahotannin da muka samu, a wasu kasashen Turai an kafa wasu dokoki na sanya mutanen gari su rika yin leken asiri a kan musulmi. Wannan dabi'a ce ta zalunci, dukkanmu mun san cewa abin da mai zalunci ya yi babu makawa zai dawo a kansa. Bugu da kari a kan haka kuma musulmi ba su cancanci wannan rashin godiya da mayar musu da mummuna ba. Turawan yamma sun san musulmi da kyau tsawon karnonin da suka gabata. A wancan lokacin da Turawan yamma suka zama baki a kasashen musulmi, sun kyalla ido da ganin irin dukiyar da masu gidan suke da su. Ko kuma a lokacin da suka zama su ne masu masaukin musulmi, sun amfana da ayyuka da kuma tunanin musulmi. A mafi yawan lokuta babu abin da suka gani daga musulmi sai kauna da abin yabawa.

A saboda haka, Ya ku matasa, ina son ku gina sahihiyar mu'amala da duniyar musulmi, bisa masaniya ta gaskiya tare da amfana da kuma ilmantuwa da gogewa mai yawa da musulmi suke da ita. Idan kuka yi hakan nan ba da jimawa ba za ku ga cewa lallai kun yi gini a kan tabbataccen tushe da zai samar muku da inuwa ta nitsuwa da tabbacin zuwa ga maginin wannan gini da kuma tabbatar masa da aminci da kwanciyar hankali da kuma bude kofar fata ta gari a doron duniya.

Sayyid Ali Khamenei
8, ga watan Azar, 1394
(28, ga watan Nuwamba, 2015)